An Sace Wani Dan Kasar Jamus A Nijar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i29848-an_sace_wani_dan_kasar_jamus_a_nijar
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce an sace wani Bajamushe da ke gudanar da ayukan jin-kai a kusa da iyakar Mali.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Apr 12, 2018 11:15 UTC
  • An Sace Wani Dan Kasar Jamus A Nijar

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce an sace wani Bajamushe da ke gudanar da ayukan jin-kai a kusa da iyakar Mali.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Alhamis, gwamnatin ta Nijar ta sanar da cewa wasu 'yan bindiga kan babura sun sace wani jami'in agaji dan kasar Jamus mai suna Joerg Lange a garin Inates na jahar Tilabery dake iyaka da kasar Mali.

An sace jami'in ne a yayin da yake komawa daga ayukan agaji a arewacin yanki, shi dai wannan yanki ya fuskanci hare-haren ta'addanci kan jami'an tsaro da fararen hula daga kungiyoyi masu da'awar jihadi da ke da alaka da al-Qaeda da Kungiyar IS.

Kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani a kan 'yan bindigar.