Rikici Ya Hallaka Mutum 24 A Kasar Afirka Ta Tsakiya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i30518-rikici_ya_hallaka_mutum_24_a_kasar_afirka_ta_tsakiya
Majiyar asibiti a kasar Afirka ta tsakiya ta sanar da mutuwar mutum 24 sanadiyar rikicin Bangui babban birnin kasar.
(last modified 2018-08-22T11:31:47+00:00 )
May 03, 2018 11:52 UTC
  • Rikici Ya Hallaka Mutum 24 A Kasar Afirka Ta Tsakiya

Majiyar asibiti a kasar Afirka ta tsakiya ta sanar da mutuwar mutum 24 sanadiyar rikicin Bangui babban birnin kasar.

Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya nakalto majiyar asibitin kasar Afirka ta tsakiya a wannan alhamis na cewa, rikicin baya-bayan na kwanaki uku da ya auku a birnin Bangui ya yi sanadiyar hallaka mutum 24.

Balkisa Ide Seidou daya daga cikin jami'an kungiyar kare hakin bil-adama na kasa da kasa a kasar ta bayyana cewa matukar dai ba a kame wadanda suka yi sanadiyar wannan tashin hankali ba, to shakka babu rikicin na iya sake barkewa a nan gaba.sannan ta nemi a gurfanar da su a gaban kotu.

Tun a shekarar 2013 ne jamhoriyar Afirka ta tsakiya ta fada cikin rikici sanadiyar rikicin kabilanci da addini.