Amurka Ta Hallaka Mayakan Al-Shabab 27 A Somaliya
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i31452-amurka_ta_hallaka_mayakan_al_shabab_27_a_somaliya
Rundunar sojin Amurka ta ce harin da dakarunta na musammam suka kai ta sama, ya hallaka mayakan al-Shabab 27 a arewacin Somaliya.
(last modified 2018-08-22T11:31:56+00:00 )
Jun 05, 2018 15:59 UTC
  • Amurka Ta Hallaka Mayakan Al-Shabab 27 A Somaliya

Rundunar sojin Amurka ta ce harin da dakarunta na musammam suka kai ta sama, ya hallaka mayakan al-Shabab 27 a arewacin Somaliya.

Sanarwar da rundunar sojin Amurka dake aiki a Afrika (AFRICOM) ta fitar, ta ce an kai harin na ranar Asabar ne da hadin gwiwar gwamnatin Somaliya, a kudu maso yammacin birnin Bosaso.

Harin dai bai shafi fararen hula ba, a cewar sanarwar ta AFRICOM..

Wannan Harin, dai shi ne na baya-bayan nan cikin jerin hare-haren da dakarun Amurka ke kaiwa kasar dake yankin kahon Afrika da hadin gwiwar dakarun Tarayyar Afrika.

Ana kai galibin ire iren wadanan hare-haren ne kan jagororin kungiyar al-Shabab da sansanoninsu dake kudancin Somaliya, inda har yanzu kungiyar ke rike da wasu yankuna.