An hallaka wani komandan 'yan ta'adda a kasar Masar
Majiyar tsaron kasar Masar ta sanar da hallaka wani komandan 'yan ta'adda na kungiyar Ajnadu Masar
A cikin wata sanarwa da Majiyar ta fitar jiya Assabar, komandan 'yan ta'addar mai suna Hamam Muhamad na Ajnadu Masar ya hallaka ne a yayin wani sumame a Dakarun tsaron kasar suka kai maboyarsa, bayan da sojojin biyu sun jikkata.
'yan kashe shekaru biyu ana neman Hamam Muhamad,inda sai a jiya Assabar aka samu nasarar hallaka shi a maboyarsa.
Ajnadu Masar wata karamar kungiyar 'yan ta'adda ce da ta dauki yaunin hare-haren baya-bayan nan da aka kai a cikin kasar ta Masar
A bangare guda ,Dakarun tsaron na Masar na ci gaba da kai sumame a yankunan Rafah, sheihu Zuwaid da Al-Arish dake Tsibirin Sina ta Arewa domin karya lagon kungiyoyin 'yan ta'adda.
Tun bayan da aka kifar da Gwamnatin Muhamad Mursi a kasar ta Masar shekarar 2013 , aka samu billar kungiyoyin 'yan ta'adda, inda suka fara kai hare-haren su kan jami'an 'yan sanda da Sojojin a tsibirin Sina ta Arewa.