Masar : Kotu Ta Sanya Sunaye Wasu 'Yan Ihwan Cikin Jerin 'Yan Ta'adda
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i33832-masar_kotu_ta_sanya_sunaye_wasu_'yan_ihwan_cikin_jerin_'yan_ta'adda
Wata kotu a birnin Alkahira na kasar Masar ta sanya sunayen 'yan kungiyar Ihwanul-Muslimin 164 cikin jerin sunayen 'yan ta'adda a kasar.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Oct 29, 2018 12:14 UTC
  • Masar : Kotu Ta Sanya Sunaye Wasu 'Yan Ihwan Cikin Jerin 'Yan Ta'adda

Wata kotu a birnin Alkahira na kasar Masar ta sanya sunayen 'yan kungiyar Ihwanul-Muslimin 164 cikin jerin sunayen 'yan ta'adda a kasar.

Wata kotu a birnin Alkahira na kasar Masar a yayin zamanta a jiya Lahadi ta sanar da cewa: A karkashin shirin yaki da ta'addanci a Masar akwai wasu 'yan kungiyar Ihawanul-Muslimin ta 'yan uwa musulmi a kasar da suke barazana ga  al'ummar Masar da 'yancinsu gami da kokarin tauyaye musu hakkokinsu, sakamakon haka kotun ta zartar da hukuncin sanya sunayensu cikin jerin gungun 'yan ta'adda a kasar.

Daga cikin 'yan kungiyar ta Ihwan 164 da aka sanya cikin jerin 'yan ta'addan har da wasu daga cikin shugabannin kungiyar ta Ihwan misalin Muhammad Islambuli, Tariq Al-Zamra, Asim Abdul-Majid, Majdi Husaini da kuma Asim Dayab.