Nijar : Boko Haram Ta Kashe Mutane 20 A Bosso
May 20, 2016 08:20 UTC
Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa 'yan kungiyar Boko Haram sun kashe akalla mutum 20 a wani hari da suka kai a garin Yebi na yankin Bosso ranar Alhamis da daddare.
Ganau sun ce mayakan kungiyar ta Boko Haram sun kuma kona kasuwa da kuma masallacin Juma'a na garin, kana akwai wasu mutane da dama
sun jikkata sanadin harin.
Tags