Nuna Damuwar Majalisar Dinkin Duniya Akan Kasar Congo
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i5578-nuna_damuwar_majalisar_dinkin_duniya_akan_kasar_congo
Majalisar dinkin duniya ta nuna damuwa akan hare-haren da ake kai wa a gabacin kasar Congo.
(last modified 2018-08-22T11:28:19+00:00 )
May 21, 2016 12:32 UTC
  • Nuna Damuwar Majalisar Dinkin Duniya Akan Kasar Congo

Majalisar dinkin duniya ta nuna damuwa akan hare-haren da ake kai wa a gabacin kasar Congo.

A jiya juma'a ne babban magatakardar majalisar dinkin duniya Bon Ki Moon ya bayyana damuwarsa akan hare-haren da sojojin gwamnatin Congo so ke kai wa a gabacin kasar.

Bon Ki Moon wanda ya ke magana ta wayar tarho da shugaban kasar congo Denis Sassou N'Guesso ya nuna damwarsa akan farmakin da jami'an tsaron su ka kai a yanin Pool da ke kudu maso gabcin kasar.

Babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniyar ya bukaci da a bai wa kungiyoyin kare hakkin bil'adama damar shiga cikin yankin.