An Kashe 'Yan ta'adda Masu Yawa A Masar
Majiyar Tsaron Masar ta tabbatar da kashe masu dauke da makamai a gabacin kasar.
Kamfanin Dillancin Labarun Kasar Jordan ya nakalto wat amajiyar tsaron kasar na cewa; A yau alhamis ne jami'an tsaron kasar ta Masar su ka kai farmaki a wata mabuya ta 'yan ta'adda a yankin Sheikh Zuwaid da ke birnin Rafah, idan su ka kashe shida daga cikinsu.
Majiyar tsaron ta Kasar masar ta ci gaba da cewa; An kuma sami wasu motoci da babura da 'yan ta'addar su kan yi amfani da su wajen kai harin, kuma tuni an lalata su.
A wani labarin na daban daga garin Rafah, sojojin masar din hudu sun mutu a yayin da su ke kokarin kwance wani bom da aka dasa a jiya laraba.
Yankin Sina ta arewa dai yana fama da matsalolin tsaro saboda tungar da 'yan ta'adda su ka yi a cikinsa.