Nijar : Boko Haram Ta Sake Kai Wani Mummunan Hari A Diffa
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i6226-nijar_boko_haram_ta_sake_kai_wani_mummunan_hari_a_diffa
Rahotanni dake cin karo da juna daga jamhuriya Nijar ne cewa 'yan boko haram sun sake kai wani mumunan hari a garin Bosso dake kusa da yankin tafkin Chadi a iyaka da Najeriya.
(last modified 2018-08-22T06:58:23+00:00 )
Jun 04, 2016 01:16 UTC
  • Nijar : Boko Haram Ta Sake Kai Wani Mummunan Hari A Diffa

Rahotanni dake cin karo da juna daga jamhuriya Nijar ne cewa 'yan boko haram sun sake kai wani mumunan hari a garin Bosso dake kusa da yankin tafkin Chadi a iyaka da Najeriya.

Harin dai na yammacin jiya Juma'a a cewar rahotanni ya cilastawa sojojin kasar janyewa daga yankin sa'o'i kadan bayan da maharan suka farbawa garin.

Saidai a cewar ministan tsaro na kasar sojojin sun ja daga ne, kuma bayan hakan sun maida martani, koda yake babu wanda ya gamsu da wannan bayanin.

Abun damuwa dai a nan shi ne dubun al'umma ke rayiwa a wurin.

ko ranar Laraba data gabata ma dai mayakan na boko haram sun farmawa garin na Bosso inda wasu rahotanni ke cewa sun kashe mutane akalla 9 tareda jikkata wani adadi mai yawa.