Afirka Ta Tsakiya: Kin Amincewar Wata Kungiya Da Aje Makaman Yaki.
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i8419-afirka_ta_tsakiya_kin_amincewar_wata_kungiya_da_aje_makaman_yaki.
Kungiyar MPC mai dauke da makamai a kasar Afirka ta tsakiya ta ki amincewa da kwance damarar yaki.
(last modified 2018-08-22T11:28:37+00:00 )
Jul 20, 2016 18:58 UTC
  • Afirka Ta Tsakiya: Kin Amincewar Wata Kungiya Da Aje Makaman Yaki.

Kungiyar MPC mai dauke da makamai a kasar Afirka ta tsakiya ta ki amincewa da kwance damarar yaki.

Kungiyar MPC mai dauke da makamai a kasar Afirka ta tsakiya ta ki amincewa da kwance damarar yaki.

Radiyon Faransa na kasa da kasa, ya ambato Abcar Sabone, mai magana da yawun kungiyar ta MPC yana fada a yau laraba cewa; Matukar ba a aiwatar da sharuddan tattaunawar  sulhu ta kasa da aka yi ba, to ba za su taba aje makamansu ba.

Sabone ya ci gaba da cewa; Har yanzu kasar tana cikin rikici saboda haka dole ne kungiyoyi su ci gaba da rike makamansu.

Maganar ta Sabone dai ta zo ne a matsayin maida martani ga jawabin da shugaban kasar Fautin Archange Touadera ya yi na kwace makaman dukkanin kungiyoyi.

Tun bayan zaben shugaban kasar da aka yi a kasar ta Afirka ta tsakiya, an sami dawowar zaman lafiya na azo a gani.