Kasashen Niger Da Aljeriya Sun Jaddada Muhimmancin Karfafa Alaka A Tsakaninsu
Gwamnatocin kasashen Niger da Aljeriya sun jaddada muhimmancin karfafa alaka da taimakekkeniya a tsakaninsu da nufin bunkasa ci gaban kasashen biyu.
A ganawar da ta gudana tsakanin ministan harkokin wajen Jamhuriyar Niger Ibrahim Yakuba da takwararsa na kasar Aljeriya Ramtane Lamamra a birnin Alges fadar mulkin kasar Aljeriya a jiya Talata: Ministocin biyu sun tattauna batutuwan da suka shafi alakar kasashen biyu tare da jaddada muhimmancin karfafa alakar jakadanci da taimakekkeniya a tsakaninsu musamman kan batun yaki da ta'addanci.
A ganawarsa da manema labarai ministan harkokin wajen Jamhuriyar Niger Ibrahim Yakuba ya bayyana cewa: Barazanar ayyukan ta'addanci da matsalar bakin haure suna daga cikin matsalolin da suke addabar kasashen Niger da Aljeriya.
Tun a shekara ta 2010 kasashen Mauritaniya, Niger, Mali da Aljeriya suka cimma yarjejeniyar hadin gwiwa a fagen fuskantar matsalolin tashe-tashen hankula da barazanar ta'addanci a tsakaninsu.