Kashe 'yan ta'adda A Kasar Masar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i8752-kashe_'yan_ta'adda_a_kasar_masar
Sojojin Masar Sun Kashe 'Yan ta'adda Masu Yawa A Kasar Masar
(last modified 2018-08-22T06:58:40+00:00 )
Jul 27, 2016 07:48 UTC
  • Kashe 'yan ta'adda A Kasar Masar

Sojojin Masar Sun Kashe 'Yan ta'adda Masu Yawa A Kasar Masar

Majiyar Tsaron Masar ta ce; Sojojin Kasar sun kashe 'yan kungiyar ta'adda ta "Ansaru Baitul-Muqaddas" masu yawa a yankin Sina ta arewa.

Tashar telbijin din al-mayadeen daga kasar Lebanon ta nakalto sojojin Masar suna fadar cewa; farmakin da su ka kai a yankin Rafah ta yamma, yayi sanadin kashe 'yan kungiyar "Ansarul-Baitul-Muqaddas" 25 tare kuma da jikkata wasu 15.

Majiyar  sojan Masar din ta ci gaba da cewa; An yi amfani da jirage masu saukar angulu samfurin Apache a kan 'yan ta'addar da su ke a garin Bal'aa a  Rafah ta yamma.

A ranar litinin din da ta gabata  an kai wani harin ta'addanci a yankin na Rafah wanda ya dauki rayukan jami'an tsaron Masar 11.