Da'esh Ta Kashe Sojojin Masar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i991-da'esh_ta_kashe_sojojin_masar
Kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ta dauki alhakin kashe sojojin Masar biyu.
(last modified 2018-08-22T06:57:50+00:00 )
Feb 19, 2016 09:12 UTC
  • Da'esh Ta Kashe Sojojin Masar

Kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ta dauki alhakin kashe sojojin Masar biyu.

Kamfanin Dillancin Labarun (AFP) ya nakalto wata sanarwa da kungiyar 'yan ta'adda ta Da'esh ( Isil) ta yi na daukar alhakin kashe wasu mutane biyu da ta bayyana a matsayin 'yan leken asirin sojan Masar.

A jiya juma da marece ne dai kungiyar ta Da'esh ta fitar da hoton da ta sanya a sahfin Twitter inda ta ke fille kawukan mutanen biyu da ta kira 'yan leken asirin sojojin da su ka yi ridda" kamar yadda ta saba kiran sojan kasar Masar.

A baya ma dai 'yan ta'addar sun sha nuna yadda su ke kashe sojojin Masar da su ke zargi da yi musu leken asiri.