Rauhani: Amurka Ce Tushen Ta'addanci A Yankin Gabas Ta Tsakiya
Shugaban Kasar Iran ya ce; Amurka ce tushen Ayyukan Ta'addanci A Kasashen wannan yankin.
Shugaban na jamhuriyar musulunci ta Iran Sheikh Hassan Rauhani, wanda ya gabatar da jawabi a yau asabar ya ce; Idan ace Amurka ba ta kai wa Afghanistan da Afghanistan hari ba, kuma ba ta kirkiri rikici a kasar Syria ba, to da ta'addanci bai watsu kamar yadda ya ke a yanzu ba.
Shugaban kasar ta Iran ya ci gaba da cewa; Wajibi ne kasashen duniya su hada karfi da karfe domin fada da ayyukan ta'addancin kungiya irin Da'esh.
Shugaba Hassan Rauhani, ya ci gaba da cewa; Yaki, yana a matsayin barna ce, amma kare kai daukaka ce ga kasa, don haka wajibi ne ga kowace kasa ta yi gwagwarmaya domin korar masu wuce gona da iri.