Tsawaita Lokacin Zabe
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i1324-tsawaita_lokacin_zabe
Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida Ta Tsawaita Loakcin Zabe
(last modified 2018-08-22T06:57:52+00:00 )
Feb 26, 2016 15:28 UTC
  • Tsawaita Lokacin Zabe

Ma'aikatar Harkokin Cikin Gida Ta Tsawaita Loakcin Zabe

Hukumar Zaben da ta ke a karkashin ma'aiaktar harkokin cikin gidan Iran, ta sanar da tsawaita lokacin kada kuri'a da sa'oi 2:a dare a dukkanin fadin kasa.

A wani bayani da ma'aiakatar ta fitar dazu ta yaba da yadda mutane su ka fito da yawa domin yin zaben 'yan majalisar shawarar musulunci da kuma majalisar kwararru, an tsawaita lokacin yin zaben da sa'oi 2 na dare.

Tun da safiyar yau juma'a ne dai miliyoyin mutane su ka fito domin zabar 'yan majalisun shawarar musulunci da kuma na kwararru. Da akwai mutane miliyan 55 da su ka cancanci kada kuri'a a Iran.