Iran: Tattaunawar Syria tana dauke da cusa fata.
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i18274-iran_tattaunawar_syria_tana_dauke_da_cusa_fata.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran ya ce; Gwarwgadon yadda gwamnati da yan hamayya su ke tattaunawa ake kara samun kyakkyawan fata.
(last modified 2018-08-22T11:29:46+00:00 )
Mar 06, 2017 12:03 UTC

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran ya ce; Gwarwgadon yadda gwamnati da yan hamayya su ke tattaunawa ake kara samun kyakkyawan fata.

Bahram Qasimi wanda ya gabatar da taron manema labaru a nan birnin Tehran, ya bada jawabi akan tambayar da aka yi masa dangane da taron Geneva akan Syria, ya ce; Tattaunawar tana ci gaba da tafiya kamar yadda ya ce; kamar yadda tattaunawar Astana ta kasance.

Kakakin ma'aikatar harkokin Wajen kasar ta Iran ya kuma tabo batun rikicin kasar Bahrain inda ya ce; Abubuwan da su ke faruwa sun shafi cikin gidan kasar ta Bahrain ne.

Kasimi ya kara da cewa; masu mulki a kasar ta Bahrain sun kasa warware matsalar da kasar ta ke ciki, don haka su ke dorawa jamhuriyar musulunci ta Iran duk wani abu da ya ke faruwa.