Rasha: Iran Tana Yaki Da Ta'addanci A Yankin Gabas Ta Tsakiya
https://parstoday.ir/ha/news/iran-i18986-rasha_iran_tana_yaki_da_ta'addanci_a_yankin_gabas_ta_tsakiya
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergie Lavrov ya bayyana kasar Iran a matsayin kasar da take yaki da ta'addanci a yankin gabas tsakiya.
(last modified 2018-08-22T06:59:53+00:00 )
Mar 31, 2017 02:11 UTC
  • Rasha: Iran Tana Yaki Da Ta'addanci A Yankin Gabas Ta Tsakiya

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergie Lavrov ya bayyana kasar Iran a matsayin kasar da take yaki da ta'addanci a yankin gabas tsakiya.

Sergie Lavrov ya bayyana hakan ne a wata zantawa da ta hada shi da mujallar National Interest ta kasar Amurka, inda ya bayyana cewa Iran tana da babban tasiri a yankin gabas ta tsakiya, kuma tana yaki da ta'addanci a yankin, kuma Rasha tana yin aiki na hadin gwiwa tare da Iran a wannan bangare, domin wanzar da sulhu da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya.

Dangane da kungiyar Hizbulla da kuma rawar da take takawa kuwa, ministan harkokin wajen kasar ta Rasha ya bayyana cewa; kungiyar Hizbullah tana taka gagarumar rawa  a fagen yaki da 'yan ta'adda, a daiai lokacin da gwamnatin Amurka da wasu daga cikin gwamnatocin larabawa na yankin suke ta hankoron ganin ganin sun taimaka ma 'yan ta'addan.