Akwai Wahala A Cimma Yarjejjeniyar Tsagaita Wuta A Siriya
Kakakin Ma'aikatar Harakokin Kasashen wajen Iran ya ce matukar Amurka ba ta dakatar da fadanta kan Siriya ba to akwai wahala a cimma yarjejjeniya tsagaita wuta a kasar
A yayin da yake amsa tambayoyin manema labarai dangane da yarjejjeniyar da kasashen Rasha da Amurka suka cimma kan tabbatar da yarjejjeniyar tsagaita a Siriya , Bahram Kasimi kakakin Ma'aikatar harakokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa ba za a yi bada tabbaci na zartar da yarjejjeniyar da aka cimma ba, saboda matukar kasar Amurka ba ta dakatar da kiyayya da kuma fatan ta a kan Gwamnatin Siriya ba to da wahala a zartar da yarjejjeniyar.
Kasimi ya kara da cewa Kasashen Iran, Rasha da Turkiya na iya nasu kokari wajen ganin an zartar da yarjejjeniyar tsagaita wuta a Siriyan to saidai idan kasar Amurka ta ci gaba da nuna kiyayyar da take yiwa Gwamnatin Siriyan, hakan na iya kawo cikas wajen zartar da yarjejjeniyar.