Limamin Tehran:Sadaukar Da Kan Yan Baya Ne Sirrin Zaman Lafiya
Wanda ya jagoranci Sallar juma'a anan Tehran ya bayyana cewa zaman lafiya da kwanciyar hankalin da ake da shi a Iran a yanzu tushensa tsayin dakar fursunonin yaki
Hujjatul-Islam Wal Muslimin Sayyid Muhammad Hassan Abu Turabi Far ya ce;A wannan lokacin tsayin dakar 'yan gwagwarmaya da fursunonin yaki sune tushen zaman lafiya a cikin kasashen Iran da Iraki da Syria.
Hujjatul-Islam Wal Muslimin Abu Turabi ya kuma ta hanyar dogaro da sadaukar da kan da maganatan su ka yi Iran tana iya warware matsalolin da take fuskanta a wannan lokacin
Limamin na Tehran ya kuma tabo halin da kasar Yemen take ciki sannan ya ce; Al'ummar duniya sun yi shiru akan bala'in da mutanen kasar su ka fada balle su ba su kariya.