Gyara Akan Furucin Ministan Harkokin Wajen Kasar Masar Akan Palasdinawa
Gyara Maganar Ministan Harkokin Wajen Masar
Ma'aikatar harkokin Wajen kasar Masar ta ce; an sauya abinda ministan harkokin wajen kasar ya fada dangane da haramtacciyar Kasar Isra'ila.
Kamfanin Dillancin Labarun Kasar Jamus, ya nakalto ministan harkokin wajen Masar Samih Shukry yana cewa; Hare-haren da 'yan sahayoniya su ka kai a bayan nan akan Palasdinawa, ba ta'addanci ba ne.
Su ma kafafen watsa labarun kasar Masar sun ambato Ministan harkokin wajen kasar tasu yana cewa; Matukar duniya ba ta bayyana ma'anar ta'addanci ba, to babu yadda za a bayyana kisan da 'yan sahayoniya su ke yi wa kananan yaran Palasdinawa, a matsayin ta'addanci.
A Palasdinu kungiyar gwagwarmayar palasdinawa ta Hamas ta maida martani akan furucin na Samih Shukry, inda kakainta Husam Badran ya ce: Mutumin da ba ya iya ganin laifukan 'yan sahayoniya to makaho ne.