Zanga-zangar Mutanen Bahrain Domin Kare Sheikh Isa Qassim
Dubban Mutanen Kasar Baharain sun yi Zanga-zangar nuna goyon bayansu ga Sheik Isa Qasim.
Dubban Mutanen Kasar Baharain sun yi Zanga-zangar nuna goyon bayansu ga Sheik Isa Qasim.
Tashar Telbijin din Lu'u,lulah ta 'yan adawar kasar Bahrain, ta bada labarin cewa; A yau juma'a dubban mutanen kasar sun gudanar da zanga-zanga a yankunan kasar daban-daban, suna masu neman a janye raba babban malamin addinin kasar da hakkin zaman dan kasa.
Masu zanga-zangar sun rika bada taken kiran mahukuntan kasar da su saki fursunonin siyasa.
Bugu da kari wasu mutanen kasar sun yi zaman dirshan a bakin gidan shehun malamin a matsayin bashi kariya daga mahukuntan kasar.
Tun a cikin watan Rebrairu na 2011 ne dai al'ummar kasar ta Bahrain su ka fara yunkurin neman samar da sauye-sauye a cikin kasar.