Masar: Fashewar Wasu Abubuwa Sun Kashe mutane 6 A Birnin Alkahira.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i15043-masar_fashewar_wasu_abubuwa_sun_kashe_mutane_6_a_birnin_alkahira.
An Kashe Mutane Shida A Wani Hari A Birnin Alkahira.
(last modified 2018-08-22T06:59:22+00:00 )
Dec 09, 2016 08:29 UTC
  • Masar:  Fashewar Wasu Abubuwa Sun  Kashe mutane 6  A Birnin Alkahira.

An Kashe Mutane Shida A Wani Hari A Birnin Alkahira.

Tashar telbijin din gwamnatin Masar ta ce; wasu abubuwa sun fashe a kusa da wata cibiyar bincike na tsaro da ke birnin alqahira.

Tashar telbijin Nile ta ce abubuwan sun fashe ne a unguwar Talibiyyah da ke cikin babban birnin.

Majiyar yan sanda ta ce; fashewar ta faru ne a dan da wurin binciken tsaro a kusa da wani masallaci.

Kawo ya zuwa yanzu babu cikakken bayani akan wadanda su ka kai harin, da kuma girman barnar da ya yi.