Masar: An daure'Yan Leken Asirin Isra'ila Zaman Kurkuku Na Har Abada.
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i18362-masar_an_daure'yan_leken_asirin_isra'ila_zaman_kurkuku_na_har_abada.
Wata kotu a kasar Masar ta daure 'yan leken asirin Haramtacciyar Kasar Isra'ila, Misrawa da yahudawa zaman kurkuku na har abada.
(last modified 2018-08-22T11:29:47+00:00 )
Mar 09, 2017 12:09 UTC
  • Masar: An daure'Yan Leken Asirin Isra'ila Zaman Kurkuku Na Har Abada.

Wata kotu a kasar Masar ta daure 'yan leken asirin Haramtacciyar Kasar Isra'ila, Misrawa da yahudawa zaman kurkuku na har abada.

Wata kotu a kasar Masar ta daure 'yan leken asirin Haramtacciyar Kasar Isra'ila, Misrawa da yahudawa zaman kurkuku na har abada.

Majiyar kotun kasar ta Masar ta sanar a jiya laraba cewa; Wasu Misrawa uku, da 'yan haramtacciyar kasar Isra'ila 6, an yanke musu zaman kurkukun ne na har abada bayan da aka same su da hannu a kan ayyukan ta'addanci.

Mutane biyu da aka yankewa hukuncin a gabansu, wato Audah Talab, Ibrahim Barham, da kuma Salamah Hamad Farhan, Abu Jarad, 'yan kasar ta Masar ne, yayin da sauran kuma basu halarcin zaman kotun ba.

Tun a 2013 ne aka bude shari'ar mutanen da aka tuhuma da leken asirin.