Jami'an Tsaron Isra'ila Sun Kame Wata 'Yar Majalisar Dokokin Palastinu
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i18366-jami'an_tsaron_isra'ila_sun_kame_wata_'yar_majalisar_dokokin_palastinu
Jami'an tsaron Haramtacciyar kasar Isra'ila sun kame wata 'yar majalisar dokokin Palastinu a yau a gidanta da ke kusa da birnin Alkhalil a gabar yamma da kogin Jordan.
(last modified 2018-08-22T11:29:47+00:00 )
Mar 09, 2017 16:52 UTC
  • Jami'an Tsaron Isra'ila Sun Kame Wata 'Yar Majalisar Dokokin Palastinu

Jami'an tsaron Haramtacciyar kasar Isra'ila sun kame wata 'yar majalisar dokokin Palastinu a yau a gidanta da ke kusa da birnin Alkhalil a gabar yamma da kogin Jordan.

Kamfanin dillancin labaran shafaqana ya bayar da rahoton cewa, Samira Al Halaiqa 'yar majalisar dokokin Palastinu ce da ke nuna rashina mincewa da zaluncin Isra'ila a kan al'ummar Palastinu, da kuma keta alfarmar wurare masu tsarki da sojojin Isra'ila ke yi.

Rahoton ya ce da jijjifin safiyar yau sojojin Isra'ila sun kai samame a kan gidanta da ke garin Al-shuyukh da ke kusa da birnin Alkhalil, inda suka fitar da ita daga cikin iyalanta, kuma suka da ita wani wuri da ba a sani ba.

Yanzu haka dai 'yan majalisar dokokin Palastinu 10 suke tsare a hannun jami'an tsaron haramtacciyar kasar Isra'ila, da suka hada har da dan majalisa guda daga kungiyar Fatah, da kuma wasu daga kungiyoyin hamas da Jabhat Sha'abiyyah.