Masar: Hizbullah Ba Kungiyar Ta'adda ba ce:
Mar 05, 2016 16:23 UTC
Jam'iyyar karamah ta masar ta yi watsi da bayyan Hizbullah a matsayin 'yar ta'adda:
Tashar telbijin din al-mayadden mai watsa shirye-shiyenta daga Beirut ta watsa wani bayani da jam'iyyar al-Karamah ta Masar ta fitar, da a cikin ta ke yi watsi da matakin kasashen larabawan yankin tekun pasha na bayyana kungiyar Hizbullah a matsayin 'yar ta'adda.
Bayanin ya ci gaba da cewa; sabanin mahangar siyasa bai kamata a ce ya sa an keta hurumi da zubar da mutuncin abokin hamayya ba.
Jam'iyyar ta alkaramah ta ce wajibi ne a rungumi kungiyoyin gwagwarmayar da ake da su a cikin wannan yankin maimakon mayar da su saniyar ware.
Tags