Hamas Ta Yi Kira Zuwa Ga Zanga-Zangar Kare Masallacin Quds
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i22440-hamas_ta_yi_kira_zuwa_ga_zanga_zangar_kare_masallacin_quds
Kungiyar Hamas ta yi kira zuwa ga gagarumar zanga-zanga a yau Juma'a a dukkanin fadin Palastinu.
(last modified 2018-08-22T11:30:25+00:00 )
Jul 21, 2017 06:31 UTC
  • Hamas Ta Yi Kira Zuwa Ga Zanga-Zangar Kare Masallacin Quds

Kungiyar Hamas ta yi kira zuwa ga gagarumar zanga-zanga a yau Juma'a a dukkanin fadin Palastinu.

Tashar talabijin ta alalam ta bayar da rahoton cewa, kungiyar gwagwarmayar Palastinawa ta Hamas ta yi kira zuwa ga gagarumar zanga-anga a yau Juma'a a dukkanin zirin Gaza da kuma yankunan gabar yamma da kogin Jordan da birnin Quds.

Bayanin ya ce manufar wannan jerin gwano a yau ita ce bayyana wa duniya halin masallacin Quds mai alfarma yake ciki a hannun yahudawa, tare da hana musulmi gudanar da sallar a cikinsa.

Haramtacciyar kasar Isra'ila tare da cikakken goyon bayan Amurka da wasu daga cikin larabawa 'yan amshin shata ga Amurka, tana ci gaba da cin karenta babu babbaka a kan al'ummar Palastine, tare da keta alfarmar wurare masu alfarma.