Palasdinu : Mutum 10 Suka Yi Shahada, Bayan Matakin Trump Kan Qudus
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i26423-palasdinu_mutum_10_suka_yi_shahada_bayan_matakin_trump_kan_qudus
Hukumomin kiwon lafiya a Palasdinu sun sanar da cewa, mutane a kalla goma ne suka yi shahada, kana wasu kimanin 2,000 suka ji raunuka a ci gaba da zanga-zangar tir da matakin shugaba Trump na Amurka kan Qudus.
(last modified 2018-08-22T11:31:09+00:00 )
Dec 17, 2017 11:11 UTC
  • Palasdinu : Mutum 10 Suka Yi Shahada, Bayan Matakin Trump Kan Qudus

Hukumomin kiwon lafiya a Palasdinu sun sanar da cewa, mutane a kalla goma ne suka yi shahada, kana wasu kimanin 2,000 suka ji raunuka a ci gaba da zanga-zangar tir da matakin shugaba Trump na Amurka kan Qudus.

Yau dai an shiga kwana goma a ci gaba da zanga-zangar ta yin Allawadai da matakin Trump na ayyana Qudus a hukumance a matsayin babban birnin yahudawan sahayoniya.

Kakakin ma'aikatar lafiya ta Palasdinu, Ashraf al-Qudra, ya ce galibin wadanda lamarin ya rusa da su an harbe su ne da harsashin bindiga, da kuma wadanda suka shaki borkonon tsohuwa na jami'an tsaron Isra'ilar.

A ranar Juma'a da ta gabata kawai, mutum hudu ne suka yi shahada a cewar hukumomin lafiya na Palasdinu.