Masar: An Tsananta Matakan Tsaro A Kusa Da Maja'miu
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i26921-masar_an_tsananta_matakan_tsaro_a_kusa_da_maja'miu
Sojojin kasar Masar ne suka sanar da daukar matakan tsaron a kusa da majami'ai bayan harin da aka kai.
(last modified 2018-08-22T07:01:13+00:00 )
Jan 01, 2018 15:29 UTC
  • Masar: An Tsananta Matakan Tsaro A Kusa Da Maja'miu

Sojojin kasar Masar ne suka sanar da daukar matakan tsaron a kusa da majami'ai bayan harin da aka kai.

Kamfanin dillancin labarun Xinhua na kasar Sin, ya ambato kakakin sojojin Masar Thamir Rufa'i ya ci gaba da cewa daukar matakan  yana da alaka ne da bukukuwan sabuwar shekarar miladiyya.

Bugu da kari, matakan sun shafi dukkanin fadinkasar ta Masar wacce take fuskantar barazanar tsaro daga yan ta'adda.

Kungiyoyin 'yan tadda masu alaka da Da'esh ne suke kai mafi yawanci hare-haren a kasar ta Masar.

A daidai lokacin da mabiyar addinin kirista suke bikin kirsimeti a Majalisar Marnina da ke kudancin alkahira an kai harin ta'addancin da ya ci rayukan mutane 10