Feb 03, 2018 18:59 UTC
  • Isma'ila Haniyyah: Muna Ci Gaba Da Riko Da Tafarkin Gwgawarmaya

Shugaban bangaren siyasa na kungiyar Hamas Isma'ila Haniyyah ya ce; Kungiyar ba za ta taba sauya matsayarta akan gwagwamaryama ba saboda wani mataki da gwamnatin Amurka ta dauka

Haniyya wanda ya gabatar da jawabi a masallacin Abyadh da ke sansanin 'yna gudun hijira na Shadhi. a yammacin zirin Gaza, ya ce; Matakin da Amurka ta dauka na mayar da ofishin jakadancinta zuwa birnin Kudus, haka nan kuma shigar da sunansa a cikin jerin 'yan ta'adda ba wani alfanu da zai jawo wa Amurkan.

Haniyyah ya kuma ce; Duk wani matakin da 'yan Sahayoniya za su dauka akan gwagwarmaya, babu abin da zai kara wa masu gwgawarmayar idan  ba tsayin daka da turjiya ba.

A ranar 31 ga watan Janairu ne dai Baitulmalin Amurka ya shigar da sunan Isma'la Haniyya a cikin  bakin littafin Amurka na wadanda take kira 'yan ta'adda.

Tags