Ministan Harkokin Wajen Turkiya Zai Kawo Ziyarar Aiki A Iran
Feb 07, 2018 12:31 UTC
A yau laraba ne ake sa ran isowar ministan harkokin wajen Turkiya inda za gana da jami'an gwamnatin Iran
Kamfanin dillancin labarun "Iran" ya ambato cewa; A yayin ziyarar ta ministan harkokin wajen Turkiyan zai gana da takwaransa na Iran Muhammad Jawad Zarif da kuma shugaban kasa Dr. Hassan Rauhani.
Bangarorin biyu dai za su tattauna alaka a katsakanin kasashensu da kuma abubuwan da suke faruwa a cikin yankin gabas ta tsakiya.
A cikin shekarun bayan nan kasashen Iran da Turkiya da kuma Rasha, suna aiki tare domin warware matsalar kasar Syria.
Tags