Gwamnatin Yahudawan Sahayoniyya Tana Ci Gaba Da Rusa Gidajen Palasdinawa
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i2827-gwamnatin_yahudawan_sahayoniyya_tana_ci_gaba_da_rusa_gidajen_palasdinawa
Majiyar Hukumar Palasdinawa ta sanar da cewa: Manyan motocin rusa gine-gine wato bulldozer sun shiga kauyen Da'na da ke gabar yammacin kogin Jordan, inda suka rusa gidajen Palasdinawa masu yawa.
(last modified 2018-08-22T06:58:01+00:00 )
Mar 23, 2016 11:58 UTC
  • Gwamnatin Yahudawan Sahayoniyya Tana Ci Gaba Da Rusa Gidajen Palasdinawa

Majiyar Hukumar Palasdinawa ta sanar da cewa: Manyan motocin rusa gine-gine wato bulldozer sun shiga kauyen Da'na da ke gabar yammacin kogin Jordan, inda suka rusa gidajen Palasdinawa masu yawa.

Babban jami'in Hukumar Cin Kwarya-Kwaryar Gashin Kan Palasdinawa da ke kula da bangaren yankunan Palasdinawa da aka mamaye a gabar yammacin kogin Jordan Ghassan Daghlis a yau Laraba ya bayyana cewa; A cikin watan da ya gabata mahukuntan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila sun tura manyan motocin bulldozer har sau uku suna zuwa kauyen Da'na da ke gabashin garin Nablus a gabar yammacin kogin Jordan, inda suke rusa gidajen Palasdinawa.

Ghassan Daghlis ya kara da cewa: Mahukuntan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila suna rusa gidajen Palasdinawan ne bisa da'awar cewa an gudanar da gine-ginen ba a kan ka'ida ba, lamarin da ya janyo daruruwan mutane da suka hada da mata da tsofaffi gami da kananan yara suka rasa makwanci a kauyen.