An Kashe Yan Ta'adda 4 A Yankin Sinaa Na Kasar Masar
Feb 21, 2018 08:16 UTC
Majiyar jami'an tsaro a yankin Sinaa na kasar Masar ta bada labarin kissan yan ta'adda 4 a yankin a yau Laraba.
Tashar talabijin ta al-alam a nan Tehran ta nakalto majiyar jami'an tsaron tana cewa sun kashe yan ta'adda 4 sun kuma kama wasu 112 a wani sumamen da suka kai masu a yankin.
Sojojin kasar Masar sun fara wani farmaki na musamman kan yan ta'adda a yankin Sinaa tun ranar 9 ga watan Afrilun da ya gabata da nufin korarsu daga yankin gaba daya.
A bisa wani bayanin da jami'an tsaro a yankin suka fitar ya nuna cewa a cikin kwanaki 10 da suka gabata sun kama mutane 417 wadanda suke tuhuma da a\kasancewa cikin yan ta'adda a yankin.
Tags