Faransa: Yariman Saudiyya Mai Jiran Gado Ya Gana Da Shugabar MKO
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i29810-faransa_yariman_saudiyya_mai_jiran_gado_ya_gana_da_shugabar_mko
Muhammad Bin Salman ya gana da jagorar kungiyar MKO mai adawa da tsarin musulunci a Iran Maryam Rajabi, a gidansa da ke birnin Paris
(last modified 2018-08-22T07:01:41+00:00 )
Apr 11, 2018 03:26 UTC
  • Faransa: Yariman Saudiyya Mai Jiran Gado Ya Gana Da Shugabar MKO

Muhammad Bin Salman ya gana da jagorar kungiyar MKO mai adawa da tsarin musulunci a Iran Maryam Rajabi, a gidansa da ke birnin Paris

Yariman na Saudiyya ya jinjinawa kungiyar ta munafikai akan rawar da suka taka a tashe-tashen hankulan da su ka faru a yammacin kasar Iran a shekarar da ta gabata, sannan ya jaddada cewa za su gaba da bai wa kungiyar tallafin kudade.

Mambobin kungiyar ta MKO da dama sun yi gangami a bakin ginin ma'aikatar harkokin wajen Faransa domin nuna goyon bayansu ga ziyarar da yariman na Saudiyya ya kai kasar ta Faransa.

A cikin kwanakin nan ne Maryam Rajabi ta yi hira da jaridar Ukkaz ta Saudiyya da a ciki ta bayyana cewa; Kungiyarta ta taka rawa a tashe-tashen hankulan da su ka faru a yammacin kasar Iran a shekarar da gabata.