Masar Ta Rufe Mashigar Rafah
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i32111-masar_ta_rufe_mashigar_rafah
Cikin wani mataki na ba zata da hukumomin kasar Masar suka dauka sun sanar da rufe mashigar Rafah na tsahon kwanaki uku.
(last modified 2018-08-22T07:02:02+00:00 )
Jun 29, 2018 07:14 UTC
  • Masar Ta Rufe Mashigar Rafah

Cikin wani mataki na ba zata da hukumomin kasar Masar suka dauka sun sanar da rufe mashigar Rafah na tsahon kwanaki uku.

Kamfanin dillancin labaran Anatolie ya habarta cewa ofishin sadarwa na mashigar Rafah dake kudancin zirin Gaza ya sanar da cewa hukumomin kasar Masar sun bayar da umarnin rufe mashigar Rafah  na tsahon kwanaki uku, wanda ya fara aiki a yau juma'a.

A cikin watan Ramadan da ya gabata ne hukumomin kasar Masar  suka bude mashigar Rafah na tsahon wata guda, sannan kuma bayan watan na Ramadana suka sake kara wa'adin wata guda, to saidai kafin watan ya cika,  hukumomin na Masar suka dauki wannan mataki na bazata.

Al'ummar yankin zirin gaza na Palastinu na bukatar bude wannan mashiga na dindin din, to saidai alakar dake tsakanin hukumomin kasar Masar da  Haramtacciyar kasar Isra'ila ya hana Masar din amsa bukatar na Palastinawa.