Shugaban Kasar Zimbabwe ya goyi bayan Kafa Kasar Palasdinu
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i4-shugaban_kasar_zimbabwe_ya_goyi_bayan_kafa_kasar_palasdinu
Shugaban Kasar Zimbabwe, Robert Mugabe ya bayyana cikakken goyon bayansa na kafa kasar Palasdinu.
(last modified 2018-08-22T06:57:44+00:00 )
Jan 30, 2016 14:05 UTC
  • Shugaban Kasar Zimbabwe ya goyi bayan Kafa Kasar Palasdinu

Shugaban Kasar Zimbabwe, Robert Mugabe ya bayyana cikakken goyon bayansa na kafa kasar Palasdinu.

Kamfanin Dillancin Labarun Associated Press ya ambato shugaba Robert Mugabe wanda ya ke gabatar da jawabi a wurin taron kungiyar tarayyar Afirka yana mai kiran shugabannin kasashen Afirka da su goyi bayan kafa 'yantacciyar kasar Palasdinu.

Shugaban kasar ta Zimbabwe ya kira yi shugabannin Afirka bayan jawabin da sugaban palasdinawa Mahmud Abbas Abu Mazin ya yi, yana mai cewa; Muryar Palasdinu tana isowa kunnuwanmu.