Hamas ta karfafa matakan tsaro a kan iyakar zirin Gaza.
Kungiyar gwagwarmayar Hamas ta Palastinu ta jibke Dakarun ta a kan iyakar zirin Gaza da Kasar Masar domin tunkarar mayakan kungiyar 'yan ta'addar ISIS.
Tashar Telbijin din Al-Arabiya ta habarta cewa bayan cimma yarjejjeniya da magabatan Masar, kungiyar gwagwarmayar Palastinu ta Hamas ta jibke Dakarunta a kan iyakar Zirin Gaza da Masar ganin yadda magabatan na Masar ke nuna damuwa dangane da yadda 'yan ta'adda ke ci gaba da kwarara a tsibirin Sina.
Baya ga haka Kungiyar gwagwarmayar ta Hamas ta samar da guraren bincike da dama a kan iyakokin biyu.
Sami Abu Zuhri, mai magana da yawun kungiyar ta Hamas ya ce maganar shigar mayakan 'yan ta'adda daga yankin zirin Gaza zuwa tsibirin Sina kage ne da farfagandar magabatan HKI ne kuma manufarsu bata alakar da ke tsakanin kungiyar Hamas da magabatan birnin Alkahira.
Abu Zuhri ya kara da cewa matakan da aka dauka domin karfafa matakan tsaro a kan iyakokin Palastinu da Masar ya biyo bayan yarjejjeniyar da aka cimma ne tsakanin magabatan kungiyar Hamas da na Masar.