Bahrain: An Kame Wani Kusa Na kare Hakkin Bil'adama.
Jun 13, 2016 08:20 UTC
Sojojin kasar Bahrain sun kame Nabil Rajab Na Kungiyar Kare Hakkokin Bil'adama.
Mai dakin mutumin da aka kame, Sumayyah Rajab, ta buga a shafinta na Internet cewa; Sojojin sun shiga sun kan karai, kuma sun yi awon gaba da mai dakinta.
Shi dai Nabil Rajabi yana daga cikin kusoshin jam'iyyun hamayyar kasar, wanda a baya ma dai an sha kamashi.
Makwanni biyu da su ka gabata mahukunta a kasar ta Bahrain sun daure Sheikh Ali Salman zaman kurkuku na shekaru 8.
Shekaru kusan 5 kenan da al'ummar kasar su ka yunkura da zummar kawo sauye-sauyen siyasa a cikin kasar, sai dai mahukunta sun yi amfani da karfi wajen murkushe su.
Tags