Amurka Ta Sake Kai Hari Kan Al-Qaida A Yemen
https://parstoday.ir/ha/news/world-i18188-amurka_ta_sake_kai_hari_kan_al_qaida_a_yemen
Rahotanni da Yemen na cewa jiragen yakin Amurka sun sake kai hari kan gidajen wasu mayakan Al-Qaida ciki har da gidan wani babban kwamandan kungiyar.
(last modified 2019-04-27T14:25:10+00:00 )
Mar 03, 2017 09:54 UTC
  • Amurka Ta Sake Kai Hari Kan Al-Qaida A Yemen

Rahotanni da Yemen na cewa jiragen yakin Amurka sun sake kai hari kan gidajen wasu mayakan Al-Qaida ciki har da gidan wani babban kwamandan kungiyar.

Kamar yadda wasu majiyoyi daga yankin suka tabbatarwa da kanfanin dilancin labaren AFP sun ce hare-haren sun rutsa da mutane da dama galibi mata da yara.

Mazauna yankin Yashbam sun ce sun kwana cikin zullumi  sakamakon hare-haren.

Ko a jiya ma Amurka ta kai ire-iren wadanan hare-haren inda bayannai ke cewa an kashe wasu kwamandan kungiyar ta Al-Qaida a reshen kasashen larabawa su 12.