Kasar Girka Ta Nuna Damuwa Akan Karuwar 'Yan Gudun Hijira
Hukumar da ta ke kula da 'yan gudun hijira ta kasar Girka ta ce a cikin watanni biyu zuwa uku na bayan nan,an sami karyuwar kwararar 'yan gudun hijirar masu yawa.
Hukumar da ta ke kula da 'yan gudun hijira ta kasar Girka ta ce a cikin watanni biyu zuwa uku na bayan nan,an sami karyuwar kwararar 'yan gudun hijirar masu yawa.
Hukumar ta ci gaba da cewa; A cikn shekarar da ta gabata mutane 500 ne su ka shiga kasar wadanda aka tsugunar da su a tsibirin Lizuwi da ke kan iyaka da Turkiya, sai dai kuma a cikin wata guda na wannan shekara mutane 1000 ne su ka shiga wannan tsibirin, sai kuma wasu 3000 a sauran tsibirun kasar.
Shugaban hukumar da ta ke kula da 'yan gudun hijirar kasar ta Grika, Dmitrys Oramples ya nuna damuwar kasarsa akan kwararar 'yan gudun hijirar.