Shugaba Holland ya soki wadanda suka sanya wuta a massalacin Musulmai
https://parstoday.ir/ha/news/world-i4573-shugaba_holland_ya_soki_wadanda_suka_sanya_wuta_a_massalacin_musulmai
Shugaban Kasar Faransa Fransois Holland ya ce ba za su amince da duk wani yunkuri na kai hari ga wani Addini a kasar ba
(last modified 2018-08-22T06:58:12+00:00 )
Apr 30, 2016 12:43 UTC
  • Shugaba Holland ya soki wadanda suka sanya wuta a massalacin Musulmai

Shugaban Kasar Faransa Fransois Holland ya ce ba za su amince da duk wani yunkuri na kai hari ga wani Addini a kasar ba

Jaridar Le figaro ta kasar Faransa ta nakalto Francois Holland shugaban kasar cikin wani bayyani da ya fitar a Yau Assabar na cewa ba za su amince da duk wani hari da za a kaiwa mabiya wani addini a kasar ba, kuma wadanda suka sanya wutar a Massalacin matukar bincike ya nuna cewa da gamgam ne za a gurfanar da su a gaban kuliya.

Francois Holland ya bayyana cewa Al'ummar kasar su mabiya Addinin Islama dake zauce a tsibirin Kurs suna aiki kafada da kafada tare da jami'an tsaro domin kare kasar.

A jiya Juma'a ne wasu Mutane da ba a san ko su waye ba, suka sanya wuta A massalacin Al'ummar musulmuin garin Ajakiso dake tsirin Kours na kasar Faransa.

Wannan wuta ta yi sanadiyar asarar mai dunbun yawa a wannan massalacin.