Ganawa A Tsakanin Ministan Harkokin Wajen Iran da Shugaban Kasar Faransa
Jun 23, 2016 13:45 UTC
Muhammad Jawad Zarif Ya Gana Da Shugaban Faransa Fransua Hollande
Ministan harkokin Wajen Iran da ya ke ziyarar aiki a kasar Faransa ya gana da shugaban kasar Fransua Hollande a yau alhamis, idan su ka tattauna ci gaban da alakar kasashen biyu ta ke samu.
Ziyarar da Ministan harkokin Wajen kasar ta Iran ya kai faransa tana a matsayin share fagen ziyarar da shugaba Hassan Rauhani zai kai ne a nan gaba.
Zarif ya bayyana karuwar tuntubar juna da ake yi a tsakanin kasashen biyu wanda zai taimaka wajen bunkasa tsaro da zaman lafiya a cikin yankin gabas ta tsakiya.
A nashi gefen shugaban kasar Faransa ya jaddada muhimmancin bubkasa alaka a tsakanin kasashen biyu ta fuskoki da dama.
Tags