Gwamnatin Masar Ta Dauki Alkawarin Warware Matsalolin Tattalin Arzikin Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/world-i9367-gwamnatin_masar_ta_dauki_alkawarin_warware_matsalolin_tattalin_arzikin_kasar
Gwamnatin Masar ta dauki alkawarin cewa da zarar ta karbi bashi a bankin bada lamuni na duniya zata fara aiwatar da gyare-gyare a harkar tattalin arzikin kasar.
(last modified 2018-08-22T06:58:44+00:00 )
Aug 09, 2016 06:27 UTC
  • Gwamnatin Masar Ta Dauki Alkawarin Warware Matsalolin Tattalin Arzikin Kasar

Gwamnatin Masar ta dauki alkawarin cewa da zarar ta karbi bashi a bankin bada lamuni na duniya zata fara aiwatar da gyare-gyare a harkar tattalin arzikin kasar.

A sanarwar da gwamnatin Masar ta fitar yana dauke da cewa: Da zarar kasar ta samu bashin kudade da yawansu ya kai dalar Amurka biliyan 12 daga Asusun bada lamuni na duniya zata fara aiwatar da gyare-gyare a harkar tattalin arzikin kasar.

Har ila yau gwamnatin Masar ta gabatar da shawara ga Majalisar Dokokin Kasar kan amincewa da shirinta na aiwatar da gyare-gyare a harkar tattalin arzikin kasar na tsawon watanni goma sha takwas.

Rahotonni sun bayyana cewa; Har zuwa yanzu akwai sabani a tsakanin gwamnatin Masar da bankin bada lamuni na duniya kan bukatar da bankin duniyan ya gabatar na rage kimar kudin kasar Masar da kuma neman jinkirta fara aiwatar da gyare-gyare a wasu bangarori masu muhimmanci da suke da alaka da tattalin arzikin kasar.