-
An Sace Wata Na'urar Kwamfutar Jami'an Tsaron Amurka Dauke Da Wasu Bayanan Sirri
Mar 18, 2017 07:52Rahotanni daga kasar Amurka sun bayyana cewar an sace wata na'urar kwamfuta ta hannu mallakar jami'an tsaron farin kaya na kasar dauke da wasu bayanai na sirri masu matukar muhimmanci a birnin New York.
-
Rasha Ta Kirayi Jakadan "Isra'ila" A Kasar Saboda Harin Da "Isra'ilan' Ta Kai Siriya
Mar 18, 2017 07:51Kasar Rasha ta kirayi jakadan haramtacciyar kasar Isra'ila a kasar don neman karin bayani dangane da keta hurumin kasar Siriya da jiragen yakin haramtacciyar kasar suka yi da kuma kai hare-hare wasu bangarori na kasar.
-
Amurka : Gwamnatin Trump Ta Daukaka Kara Kan Soke Dokar Baki
Mar 18, 2017 02:23Gwamnatin shugaba Donald Trump na Amurka ta daukaka kara kan sokewar da wani alkalin kotun tarayya na yankin Maryland ya yiwa sabuwar dokar hana 'yan gudun hijira da musulmin wasu kasashe shida shiga kasar.
-
An Cafke Masu Alaka Da Da'eh 15 A Marocco
Mar 18, 2017 02:22Hukumomi a kasar Marocco sun sanar da cafke mutane 15 da ake zargi da alaka da kungiyar 'yan ta'adda ta da'esh.
-
Jaridar Independent Ta Buga Makala Da Ke Sukar Dokar Hana Saka Lullubi A Turai
Mar 17, 2017 13:46Jaridar Independent ta kasar Birtaniya, kuma daya daga cikin manyan jaridu na nahiyar turai, ta buga wata makala da ke yin kakkausar suka dangane da okar hana mata musulmi saka lullubi a wuraren aikinsu a cikin kasashen a nahiyar.
-
Sojojin Siriya Sun Fatattakin Wani Jirgin Yakin H.K. Isra'ila Da Ya Shigo Kasar
Mar 17, 2017 05:55Sojojin saman Siriya sun harba wasu makamai masu linzami kan wasu jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra'ila da suka shigo kasar da nufin kai wasu sabbin hare-hare kan wasu yankuna na kasar Siriyan.
-
Babban Sakataren MDD Ya Bayyana Damuwa Kan Karuwar Fataucin Bil'adama A Duniya
Mar 17, 2017 05:55Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana tsananin damuwarsa dangane da yadda ake ci gaba da samun karuwar fataucin mutane a bangarori daban-daban na duniya.
-
Turai Ta Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Da Ake yi Wa Musulmin Rohinga
Mar 17, 2017 03:07Tarayyar Turai ta rubuta daftarin kudurin da zai bukaci a fara bincike kan azabtar da musulmin Rohinga na Kasar Myanmar.
-
An kai hari kan ofishin Asusun bada lamini na Duniya a Faransa
Mar 16, 2017 14:21Jami'an 'yan sanda sun sanar da fashewar wani abu a ofishin Asusun bada lamani na Duniya dake birnin Paris na kasar Faransa
-
Shugaban Masu Adawa Da Musulunci Na Kasar Holland Ya Sha Kaye A Zabe
Mar 16, 2017 07:45Rahotanni daga kasar Holland sun bayyana cewar shugaban jam'iyyar PVV mai adawa da Musulunci Geert Wilders ya sha kaye a zaben da aka gudanar a kasar bayan da jam'iyyar masu sassaucin ra'ayi mai mulki a kasar ta samu gagarumin rinjaye.