-
Shugabannin ECOWAS Ba Su Amince Da Ba Wa Jammeh Kariya Ba
Jan 23, 2017 07:39Ministan harkokin wajen kasar Senegal Mankeur Ndiaye ya bayyana cewar shugabannin kungiyar tattalin arzikin kasashen Yamamcin Afirka (ECOWAS) ba su amince da batun ba wa tsohon shugaban kasar Gambiya, Yahya Jammeh kariya ba.
-
Jandarmomi Masu Bore Sun Rufe Babbar Tashar Ruwan Ivory Coast
Jan 18, 2017 14:02Rahotanni daga kasar Ivory Coast sun bayyana cewar Jandarmomi masu bore sun kwace babbar tashar jiragen ruwan kasar a yau din nan Laraba da kuma tilasta wa kamfanonin da suke wajen ciki kuwa har da kamfanonin da suke sarrafa Cocoa rufe kamfanonin na su, lamarin da ke nuni da cewa har ya zuwa yanzu dai ba a kawo karshen boren da jami'an tsaron suke yi ba.
-
Sabon Bore Sojoji A Kasar Ivory Coast
Jan 18, 2017 02:52Wani sabon bore Sojoji ya sake barkewa a kasar Ivory Coast, kwanaki kadan bayan cimma wata yarjejeniya da sojojin da suka yi bore a Bouake.
-
Gwamnatin Djibouti Zata Gina Babbar Cibiyar Kasuwanci Da Babu Kudin Fito A Kasar
Jan 17, 2017 04:51Gwamnatin Djibouti ta sanar da fara gudanar da ginin babbar cibiyar kasuwanci da babu kudin fito wato free trade zone mafi girma a nahiyar Afrika.
-
Ivory Coast : Kablan Ducan, Ya Yi Rantsuwar Kama Aiki
Jan 16, 2017 12:19Tsohon firaministan kasar Ivory Coast, Daniel Kablan Duncan, ya yi rantsuwar kama aiki a matsayinsa na mataimakin shugaban kasar.
-
Ana Gudanar Zaman Shugabannin Afirka Da Faransa A Mali
Jan 14, 2017 08:35An fara gudanar da zaman shugabannin kasashen Afirka da Faransa karo na ashirin da bakwai a birnin Bamako na kasar Mali.
-
Taron Faransa Da Kasashen Afrika A Mali
Jan 14, 2017 02:54Shugabannin kasashen Afrika na gudanar da taro tare da Faransa a birnin Bamako na Mali inda za su tattauna yaki da ta’addanci da kuma hanyoyin inganta dimokuradiya.
-
Gambia : Adama Barrow, Ya Nufi Mali Tare Da Tawagar ECOWAS
Jan 14, 2017 02:53Zababben shugaban kasar Gambia Adama Barrow, ya nufi kasar Mali tare da tawagar shiga tsakani ta kungiyar ECOWAS inda zasu halarci taron Faransa da kasashen Afrika.
-
Matsalar Kiwan Lafiya Na Bijirowa Wadanda Suka yi Jinyar Ebola
Jan 14, 2017 02:53Wani bincike na masana sha'anin kiwan lafiya ya nuna cewa uku daga cikin hudu na mutanen da suka yi jinyar cutar Ebola na fama da matsalar kiwan lafiya.
-
Ivory Coast : An Cimma Yarjejeniyar Karshe Da Sojoji Masu Bore
Jan 14, 2017 02:52Rahotanni daga kasar Ivory Coast na cewa gwamnatin kasar ta cimma yarjejeniyar karshe da sojoji da ke bore akan batun biyan albashi da kuma alwasus, bayan da ake sake shiga halin rashin tabas a Birnin Bouake inda sojojin suka kwashe wunin jiya suna harbe-harbe.