Ivory Coast : Kablan Ducan, Ya Yi Rantsuwar Kama Aiki
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i16690-ivory_coast_kablan_ducan_ya_yi_rantsuwar_kama_aiki
Tsohon firaministan kasar Ivory Coast, Daniel Kablan Duncan, ya yi rantsuwar kama aiki a matsayinsa na mataimakin shugaban kasar.
(last modified 2018-08-22T06:59:33+00:00 )
Jan 16, 2017 12:19 UTC
  • Mista Daniel Kablan Ducan, lokacin da yake rsantsuwar kama aiki (hoto AFP)
    Mista Daniel Kablan Ducan, lokacin da yake rsantsuwar kama aiki (hoto AFP)

Tsohon firaministan kasar Ivory Coast, Daniel Kablan Duncan, ya yi rantsuwar kama aiki a matsayinsa na mataimakin shugaban kasar.

A jawabin da ya gabatar yayin rantsar dashi, Mr Kablan ya ce a shirye yake ya dafawa gwamnatin Alhasan Watara domin cimma manufofinta.

Mr Kablan dan shekaru 73 a duniya wanda aka zaba karon farko a watan daya gabata a matsayin dan majalisa a yankin Grand-Bassam dake kudancin kasar, shi ne dai mutum na farko daya fara rike mukamin mataimakin shugaban kasa a wannan kasar ta Ivory Coast.

kirkiro da mukamin mataimakin shugaban kasa, wanda shi ne mukami na biyu mafi girma a kasar ta Ivory Coast, na kunshe ne a cikin sabon kundin tsarin mulkin kasar da gwamnatin Shugaba Alhasan Watara ta gabatar wanda ya samu amuncewa daga al'ummar kasar.

A ranar 9 ga watan nan ne Mr Daniel Kablan Duncan, ya gabatar da murabus din gwamnatinsa ga shugaba Watara domin share fagen nada shi a matsayin mataimakin shugaban kasa, inda kuma aka maye gurbinsa da tsohon sakatare janar a fadar shugaban kasa Amadu Gon Kulibaly wanda aka nada firaminista a yanzu.