Yajin Aikin Kwararrun Likitoci Na Kwana Biyar A Nijar
Aug 25, 2016 07:38 UTC
Likitocin Jamhuriyar Nijar Suna Yajin Aiki
Cibiyar Watsa Labaru Ta "Africa Times" daga birnin Yamai a Nijar ta ambato cewa; Kwararru liktoci sun shiga yajin aiki na kwana biyar daga jiya laraba.
Majiyar ta ce; yajin aikin ya haddasa tsaiko wajen tafiyar da ayyuka a manyan asibitoci biyu mallakin gwmanati da kuma wuraren bada magani a birnin na Yamai.
Shekaru biyu kenan ajere da kungiyar likitoci a jamhuriyar ta Nijar ta ke takkaddama da gwamnati akan batun karin albashi da kuma na karin ilimi.
Tags