Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Bukatar Samun Zaman Lafiya A Kasar Gabon
Kakakin babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya jaddada bukatar nisantar duk wani abin da zai janyo tashe-tashen hankula sakamakon sabanin siyasa a kasar Gabon.
A bayanin da ya fitar a yau Talata Kakakin babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Stephane Dujarric ya yi kira ga dukkanin jam'iyyun siyasa a kasar Gabon da su dauki matakin mutunta sakamakon zaben shugabancin kasar da Hukumar zabe zata sanar tare da nisantar duk wani abin da zai janyo bullar tashe-tashen hankula a kasar.
Stephane Dujarric ya kara da cewa: Mutunta sakamakon zaben shugabancin kasa a Gabon ita ce kawai zata kai ga zaman lafiya da mutunta tsarin dimokaradiyya a kasar, sannan duk mai korafi kan sakamakon zaben ya bi hanyar doka domin neman hakkinsa.
Tuni dai Jean Ping daga cikin 'yan adawar kasar ta Gabon ya shelanta nasararsa a zaben shugabancin kasar, yayin da magoya bayan shugaban kasar ALi Bango suke ci gaba da murnar lashe zaben da ake sa- ran sanar da sakamakonsa a yau Talata.