Bukatar Shugaban kungiyar Alkalan kasar Gabon daga Magabatan Shara'ar kasar
Shugaban kungiyar Alkalan kasar Gabon ya bukaci magabatan mashara'antar kasar da su kare hakin Mutanan da aka kama sanadiyar tashe-tashen hankulan bayan zabe.
Kamfanin dillancin labaran kasar Faransa ya nakalto Jean-Pierre Eva Luna Shugaban kungiyar Lauyoyin Kasar Gabon a jiya Assabar na cewa muna bukatar Jami'an tsaro gami da masu shara'a da su yi mu'amar mai kyau da wadanda aka kame sandiyar tashe-tashen hankulan bayan zabe.
Jean-Pierre Eva Luna ya ce daga lokacin da aka bayyana sakamakon zaben shugabancin kasar a ranar Larabar da ta gabata zuwa yanzu kimanin Mutane 800 aka kame a birnin Livraville , a sauren yankunan kuma sama da Mutane 300 aka kame kuma dukkanin su na cikin mawuyacin hali a gidajen yarin da ake tsare da su.
Shugaban Lauyoyin ya kara da cewa a halin da ake ciki Lauyoyin kalilan ne suka samu damar ganawa da wadanda ake tsare da su din, kuma ya zuwa yanzu, a birnin Livraville kawai Lauyoyi 120 suka suka rubuta sunan su domin kare wadanda aka kaman.