Kotu A Mauritaniya Ta Yanke Hukuncin Dauri Kan 'Ya'yan Tsohon Shugaban Kasar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10663-kotu_a_mauritaniya_ta_yanke_hukuncin_dauri_kan_'ya'yan_tsohon_shugaban_kasar
Wata kotu a kasar Mauritaniya ta yanke hukunci dauri a gidan kurkuku kan 'ya'yan tsohon shugaban kasar bayan ta same su da laifin fataucin muggan kwayoyi.
(last modified 2018-08-22T06:58:53+00:00 )
Sep 06, 2016 01:10 UTC
  • Kotu A Mauritaniya Ta Yanke Hukuncin Dauri Kan 'Ya'yan Tsohon Shugaban Kasar

Wata kotu a kasar Mauritaniya ta yanke hukunci dauri a gidan kurkuku kan 'ya'yan tsohon shugaban kasar bayan ta same su da laifin fataucin muggan kwayoyi.

Majiyar shari'ar kasar Mauritaniya ta sanar da cewa: Kotun da ke birnin Nouakchott fadar mulkin kasar ta yanke hukuncin dauri a gidan kurkuku na tsawon shekaru 15 da kuma 6 kan Sidi Muhamed Wuld Haidalla da Sheikh Wuld Haidalla 'yayan tsohon shugaban kasar ta Mauritaniya Mohammed Khouna Wuld Haidalla bayan ta same su da hannu dumu -dumu a harkar fataucin muggan kwayoyi.

Muhammed Khouna Wuld Haidalla ya rike shugabancin Mauritaniya daga shekara ta 1980 zuwa 1984 miladiyya.

Sauran mutanen da suke da hannu a hada -hadar muggan kwayoyin an daure wasu shekaru 11 zuwa 9 musamman saboda rashin cikakkun shaidu kan sauran zarge-zargen da ake yi kansu.