Shugaban Angola Ya Tsige Ministan Kudin Kasar Daga Kan Mukaminsa
Fadar shugaban kasar Angola ta sanar da cewa: Shugaba Jose Eduardo dos Santos ya tsige ministan kudin kasar daga kan mukaminsa biyo bayan matsalar tattalin arziki da Angola ta shiga sakamakon faduwar farashin man fetur a duniya.
Babu wani kwakkwaran dalili da fadar shugaban kasar ta gabatar kan tsige ministan kudin kasar Armando Manuel dan shekaru 44 a duniya daga kan mukamin nasa bayan tsawon shekaru uku da yayi yana rike da mukamin minista.
A bayan sanar da tsige Armando Manuel an maye gurbinsa da Augusto Archer dan shekaru 53 a duniya kuma tsohon shugaban Hukumar kula da sanya hannun jari a kasar.
Tun bayan faduwar farashin dayen man fetur a kasuwannin duniya kasar Angola kamar saurar kasashen da suka dogara da mai a harkar tattalin arzikin kasarsu ta shiga cikin masifar tattalin arziki tare da faduwar darajar kudin kasar warwas a gaban dalar Amurka lamarin da ya kara wurga al'ummar Angola cikin tsananin rayuwa, kuma tun a cikin watan Yunin wannan shekara gwamnatin kasar ke zawarcin Bankin Bada Lamuni na Duniya na {IMF} kan neman bashin kudade da nufin rage radadin matsalar tattalin arzikin kasar.